Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya yi tir da kakkausar murya dangane da harin da aka kai da ya yi sanadin zubar da jini da ya salwantar da rayukan jama’a a kauyen Heipang da ke karamar hukumar Barkin-Ladi da sanyin safiyar Alhamis.
Wata sanarwa da Daraktan yada labarai da hulda da jama’a, Gyang Bere ya fitar ta ce gwamnan ya kuma yi Allah wadai da kashe-kashen da aka yi a wasu kauyukan karamar hukumar Mangu da aka yi a baya-bayan nan.
Gwamna Mutfwang ya bukaci jami’an tsaro da su kara zage damtse wajen kawo karshen kashe-kashen da ake yi wa mutanen da ba su ji ba gani ba gani ba a kauyukan kananan hukumomin Mangu da Barkin-Ladi na jihar.
Ya koka da tabarbarewar tsaro a wasu sassan jihar, ya kuma yi kira da a kara hada kai tsakanin shugabannin al’umma da jami’an tsaro domin kawo karshen hare-haren “marasa hankali”.
Gwamna Mutfwang ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da hadin kai a tsakanin dukkan ‘yan kasa, ba tare da la’akari da addini ko kabila ba, domin samar da zaman lafiya da ci gaban jihar.
Ya ba da tabbacin gwamnati ta himmatu wajen magance matsalolin tare da nuna juyayi ga al’ummomin da abin ya shafa da iyalan wadanda suka mutu.
Ya yi addu’ar Allah ya jikan al’ummar Heipang da Mangu da ke cikin makoki sannan ya bukace su da su yi amfani da cibiyar tsaro da bayanai da gwamnatin jihar ke aiki domin isar da bayanan tsaro domin a gaggauta shiga tsakani domin dakile afkuwar hare-haren nan gaba.