Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif ya yi alla-wadai da harin ƴanbindiga a wani masallaci da ke garin Kokorou a Jamhuriyar Nijar, inda suka kashe masallata masu dama.
A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Sharif ya bayyana harin a matsayin “abin takaici”, sannan ya ƙara da cewa “musamman ganin yadda aka kashe mutane suna sallah a watan Ramadan mai alfarma. Wannan ya ƙara nuna cewa ta’addanci ba shi da addini, kuma babu tausayi a ciki,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, “a madadin ƴan ƙasar Pakistan, muna alla-wadai da wannan harin na dabbanci, sannan muna taya ƴan Jamhuriyar Nijar baƙin ciki da jaje,” in ji shi.
Rahotanni dai na cewa aƙalla mutum 44 ne ƴanbindiga suka kashe, sannan suka jikkata gommai a harin, wanda suke kai a wani masallaci da ke garin na Kokorou.