fidelitybank

Tirƙashi: Ƴan bindiga sun sace Kwamishina yaɗa labaran jihar Binuwai

Date:

Gwamnatin jihar Benue ta tabbatar da sace kwamishinan yaɗa labarai da al’adu da yawon shaƙatawa, Matthew Abo da kuma tsohon shugaban karamar hukumar Ukum, Iorwashima Erukaa.

Babban Sakataren yaɗa labarai na gwamnan jihar, Tersoo Kula, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, ya ce wasu ‘yan bindiga ne suka yi garkuwa da Abo a gidansa da ke Sankara da misalin karfe takwas na daren Lahadi, yayin da aka yi garkuwa da Erukaa a ranar Asabar.

“Ƴan bingidar da suka yi garkuwa da mutanen biyun da har yanzu ba a san inda suke ba, sun tuntubi iyalan Erukaa amma har yanzu ba su tuntubi dangin Abo ba,” in ji sanarwar.

“Gwamnan wanda ya bayyana lamarin a matsayin abin Allah-wadai kuma abin da ba za a amince da shi ba, tuni ya umarci hukumomin tsaro da su fara aiki nan take domin ganin an sako mutanen biyu cikin koshin lafiya.”

Gwamnan ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su kwantar da hankalinsu, domin gwamnatinsa za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin jihar ta kasance mai aminci ga kowa.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp