fidelitybank

Tinubu zai yi ganawa ta musamman da shugabannin tsaro

Date:

Rahotanni na nuna cewa, shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu na shirin yin wata ganawa da hafsoshin tsaron ƙasar kan kashe-kashe a jihohin Filato da Benue da wasu sassan ƙasar.

Ganawar na zuwa ne bayan komawar shugaba Tinubu Najeriyar, bayan kwashe makonni biyu yana ziyarar aiki a Paris, babban birnin Faransa.

Ana sa ran ganawar za ta sake duba ƙarin tashin hankalin da ake samu da kuma matakan magance su.

Hakan na zuwa ne a yayin da gwamnatin ƙasar ke ɗora laifin ƙarin kashe-kashen da ake samu a kan gwamnonin jihohi.

Gwamnatin tarayyar na ɗora alhakin hakan kan rashin sanya kuɗaɗe kamar yadda ya kamata a cibiyoyin tsaron da ke jihohi duk da ɗumbin kuɗaɗen da ake warewa domin yin hakan.

Matsalar tsaro na ci gaba da zama babban ƙalubale ga hukumomin tsaro a ƙasar, lamarin da ke sanadiyyar mutuwar dubban rayuka.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp