fidelitybank

Tinubu zai yi ganawa ta musamman da shugabannin tsaro

Date:

Rahotanni na nuna cewa, shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu na shirin yin wata ganawa da hafsoshin tsaron ƙasar kan kashe-kashe a jihohin Filato da Benue da wasu sassan ƙasar.

Ganawar na zuwa ne bayan komawar shugaba Tinubu Najeriyar, bayan kwashe makonni biyu yana ziyarar aiki a Paris, babban birnin Faransa.

Ana sa ran ganawar za ta sake duba ƙarin tashin hankalin da ake samu da kuma matakan magance su.

Hakan na zuwa ne a yayin da gwamnatin ƙasar ke ɗora laifin ƙarin kashe-kashen da ake samu a kan gwamnonin jihohi.

Gwamnatin tarayyar na ɗora alhakin hakan kan rashin sanya kuɗaɗe kamar yadda ya kamata a cibiyoyin tsaron da ke jihohi duk da ɗumbin kuɗaɗen da ake warewa domin yin hakan.

Matsalar tsaro na ci gaba da zama babban ƙalubale ga hukumomin tsaro a ƙasar, lamarin da ke sanadiyyar mutuwar dubban rayuka.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp