fidelitybank

Tinubu zai tafi Hadadiyar Daular Larabawa

Date:

Shugaban kasa Bola Tinubu, zai tafi ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa domin halartar taron ɗorewar tattalin arziki na duniya ta 2025 (ADSW 2025).

Shugaban ƙasar, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan ne ya gayyaci shugaba Tinubu domin halartar taron – wanda zai gudana tsakanin 12 zuwa 18 ga watan Janairu.

Taron – wanda zai samu halartar manyan shugabannin duniya, da masana da ƙungiyoyin fararen hula da ‘yan kasuwa da masu ruwa da tsaki – zai tattauna nasarorin da aka samu a fannin tattalin arziki da zamantakewa, tare da lalubo hanyoyin ɗorewar ci gaban da aka samu.

Cikin sanarwar bulaguron da fadar shugaban Najeriya ta fitar, ta ce a taron Shugaba Tinubu zai jaddada manufofin gwamnatinsa, ciki har ci gaban tattalin arziki da makamashi da sufuri da fannin lafiya.

Haka kuma tawagar Najeriya a taron za ta gana da fadar sarkin ƙasar domin tattauna batutuwan da suka shafi ƙasashen biyu.

Ministan harkokin wajen ƙasar, Ambassador Yusuf Tuggar na daga cikin manyan jami’an gwamnatin da za su yi wa shugaban rakiya a taron, a cewar sanarwar.

Ana sa ran shugaban zai koma Najeriya bayan kammala taron ranar 16 ga watan Janairu.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp