fidelitybank

Tinubu zai tafi Faransa ziyarar aiki

Date:

Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai bar Najeriya a ranar Laraba domin kai ziyarar aiki Faransa, inda zai yi kusan makonni biyu.

Haka na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun mataimaki na musamman ga shugaban ƙasar kan harkokin watsa labarai, Bayo Onanuga.

Shugaban ya ce zai yi amfani da lokacin ziyarar don yin nazari kan yadda gwamnatinsa ta kasance a yayin da ta ke gab da cika rabin zango.

Haka kuma zai duba manyan nasarorin da gwamnatin ta samu tare da duba garonbawul ɗin da ya yi da gaggauta ci gaban da ya ke so a samu a shekara da ke tafe.

Sanarwar ta bugi ƙirji da nasarar da ta ce gwamnatinsa ta samu a fannin tattalin arziki, inda ta bayar da misali da bunƙasar asusun ajiyar kuɗaɗen waje da babban bankin ƙasar ya ce ya kai $23.11 biliyan.

Idan aka kwatanta da $3.99 biliyan da suka ce sun tarar a shekarar 2023.

Shugaban ya bayyyana cewa zai ci gaba da jagorantar al’amuran gwamnatin Najeriya, a yayin da yake Paris.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp