fidelitybank

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Date:

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan sabbin dokokin sauya tsarin haraji na ƙasar a yau Alhamis, a wani mataki da ake sa ran zai sauya tsarin tattara haraji da kuma inganta yanayin kasuwanci a Najeriya.

Sanarwar da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta hannun mai taimaka masa kan yaɗa labaru, Bayo Onanuga ta ce sabbin dokokin huɗu sun haɗa da dokar haraji ta ƙasa da dokar tafiyar da lammuran haraji da dokar kafa hukumar haraji ta Najeriya da kuma dokar kafa ma’aikatar kula da hukumomin tattara haraji ta Najeriya.

Majalisar Dokoki ta kasa ce za ta amince da su bayan shawarwari da dama daga masu ruwa da tsaki.

Sabbin dokokin harajin na Najeriya sun tayar da ƙura sosai a lokacin da shugaban ƙasar ya gabatar da su ga majalisar dokokin ƙasar, lamarin da ya kai ga dakatar da tattaunawa a kan su a zauren majalisar.

Tun da farko gwamnonin jihohin ƙasar da majalisar kula da tattalin arziƙi ta Najeriya da ƙungiyoyi sun buƙaci a sake duba dokar kafin sake gabatar da ita.

Daga baya gwamnonin jihohin ƙasar sun gudanar da gyare-gyare kan dokar tare da gabatar wa shugaban ƙasa, wanda ya amince da su kafin majalisar dokokin ƙasar ta ci gaba da muhawara.

Majalisar dokokin ƙasar ta ce a halin yanzu an gyara duk wasu ɓangarori da suka haifar da tayar da jijiyoyin wuya.

Sai dai har yanzu al’umma da dama ba su da cikakkiyar masaniyar abubuwan da dokokin suka ƙunsa.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...
X whatsapp