fidelitybank

Tinubu zai samu ruwan kuri’u a Ebonyi – Dan Majalisa

Date:

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Ezza ta Kudu/Ikwo a majalisar tarayya ya bada tabbacin cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Ahmed Bola Tinubu ne zai samu mafi yawan kuri’u a zaben 2023 a jihar Ebonyi.

Ogah ya bayyana haka ne a mahaifarsa da ke unguwar Item Amegu a karamar hukumar Ikwo ta jihar Ebonyi a yayin bikin Kirsimeti.

Ya kuma bukaci al’ummar mazabar sa da su zabi dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC tare da yin barazanar cewa ba za su ga jam’iyyun adawa ba a kasar Ikwo.

A cewarsa: “Duk wanda ya zo nan sai ya koma gida da buhun shinkafa. Da wannan ya zama dole kowa ya zabi shugaban kasarmu mai jiran gado, Ahmed Bola Tinubu domin shi ne zai samu mafi yawan kuri’u a jihar Ebonyi a zaben 2023.

“Idan aka yi haka, za mu iya tsayawa tsayin daka a majalisar dokokin kasar don neman a kara mana mukami daga shugaban kasa. Za mu zabi dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC tun daga dan takarar gwamnan mu, Ogbonnaya Nwifuru.

“Na tsaya tare da shi (Nwifuru) kuma daga yau ba na son ganin jam’iyyun adawa a kasar Ikwo. Kuka kukan hanyoyi kuma na baku hanyoyi. Kun yi kuka na sha ruwa na ba ku ruwa. Kun yi kukan neman aikin yi na ba ‘ya’yanku maza da ‘ya’yanku aikin yi. Don haka sai ku zabi ‘yan takarar APC,” inji shi.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp