Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Ezza ta Kudu/Ikwo a majalisar tarayya ya bada tabbacin cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Ahmed Bola Tinubu ne zai samu mafi yawan kuri’u a zaben 2023 a jihar Ebonyi.
Ogah ya bayyana haka ne a mahaifarsa da ke unguwar Item Amegu a karamar hukumar Ikwo ta jihar Ebonyi a yayin bikin Kirsimeti.
Ya kuma bukaci al’ummar mazabar sa da su zabi dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC tare da yin barazanar cewa ba za su ga jam’iyyun adawa ba a kasar Ikwo.
A cewarsa: “Duk wanda ya zo nan sai ya koma gida da buhun shinkafa. Da wannan ya zama dole kowa ya zabi shugaban kasarmu mai jiran gado, Ahmed Bola Tinubu domin shi ne zai samu mafi yawan kuri’u a jihar Ebonyi a zaben 2023.
“Idan aka yi haka, za mu iya tsayawa tsayin daka a majalisar dokokin kasar don neman a kara mana mukami daga shugaban kasa. Za mu zabi dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC tun daga dan takarar gwamnan mu, Ogbonnaya Nwifuru.
“Na tsaya tare da shi (Nwifuru) kuma daga yau ba na son ganin jam’iyyun adawa a kasar Ikwo. Kuka kukan hanyoyi kuma na baku hanyoyi. Kun yi kuka na sha ruwa na ba ku ruwa. Kun yi kukan neman aikin yi na ba ‘ya’yanku maza da ‘ya’yanku aikin yi. Don haka sai ku zabi ‘yan takarar APC,” inji shi.