Shugaba Bola Tinubu a ranar Litinin zai rantsar da sabbin ministoci bakwai.
Za a gudanar da rantsarwar ne a zauren majalisar dokoki da ke Abuja.
Da yake bayyana hakan ta hanyar X, mai ba Tinubu shawara na musamman kan Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya rubuta: “Shugaba Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministoci bakwai gobe Litinin.
“Minitocin su ne Dr Nentawe Yilwatda – Ministan Agaji da Rage Talauci; Muhammadu Dingyadi – Ministan Kwadago da Aiki; Bianca Odumegwu-Ojukwu – Karamin Ministan Harkokin Waje.
“Sauran su ne Dr Jumoke Oduwole – Ministan Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari (Ciniki da Zuba Jari), Idi Maiha – Ministan Dabbobi; Yusuf Ata – karamin ministan gidaje da raya birane; da Dr Suwaiba Ahmad – Karamar Ministar Ilimi.
“Majalisar dattawa ta wanke ministocin a makon da ya gabata.”
A ranar 23 ga watan Oktoba, Tinubu ya sake nada ministoci 10 a matsayin sabbin ministoci, ya sallami wasu biyar sannan ya nada sabbin ministoci bakwai.
A ranar 31 ga Oktoba, 2024, majalisar dattijai ta tabbatar da dukkan mutane bakwai da aka tantance bayan tantance kowanne.