fidelitybank

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Date:

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga al’ummar ƙasar da misalin ƙarfe 7 na safe a ranar Alhamis domin bikin ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2025.

Cikin wata sanarwa da kwamitin shirya bikin ranar Dimokradiyyar ya fitar, ya ce da rana kuma Tinubu zai halarci zaman haɗin gwiwa da ƴan majalisar dokokin ƙasar.

Sai dai sanarwar ta bayyana cewa ba za a gudanar da taron faretin ranar ba a bana. A maimakon haka, za a gudanar da muhawarar jama’a a ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa da ƙarfe 4 na yamma.

Bikin na bana na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke cika shekara 26 ƙarƙashin mulkin dimokradiyya ba tare da katsewa ba tun bayan kawo ƙarshen mulkin soja a 1999.

A baya ana bikin ranar dimokradiyya a ranar 29 ga Mayu, wadda ke zama ranar rantsar da shugabannin ƙasa da gwamnoni da kuma ƴan majalisar tarayya da na jihohi.

Amma daga shekarar 2018, an sauya ranar zuwa 12 ga Yuni domin girmama zaɓukan 1993 da aka soke – da MKO Abiola ya lashe – zaɓen da ake ganin mafi sahihanci a tarihin Najeriya.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp