fidelitybank

Tinubu zai kaddamar da aiki a lokacin da ya cika shekara a mulki

Date:

Shugaba, Bola Tinubu zai fara bikin murnar cikarsa shekara guda a kan karagar mulkin ƙasar da buɗe wasu muhimman ayyukan gwamnatin Tarayya a Legas da aka kammala a lokacin mulkinsa.

Cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban kan kafofin yaɗa labarai na zamani, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce a yau Lahadi shugaba Tinubu zai buɗe wani babban titin da aka yi da kankare zuwa manyan tasoshin jiragen ruwa na Apapa da Tin Can a birnin na Legas.

Sanarwar ta ce an fara muhimmin aikin titin ne a zamanin tsohuwar gwamnati Muhammadu Buhari da ta gabata, inda kamfanin Dangote ya ɗauki nauyi gudanar da aikin ta hanyar harajin da yake tara wa gwamnati.

”Haka kuma shugaba Tinubu zai buɗe fitacciyar gadar nan ta ‘Third Mainland’ da ta ɗauki hankali sakamakon yadda aka zamanantar da ita”, in ji Sanarwar.

”Shugaban ƙasar zai kuma ƙaddamar da katafaren aikin titin da ya tashi daga Legas zuwa Calaba da aka yi ƙiyasin cewa zai laƙume kusan naira tiriliyan 15, muhimmin titi ne da zai ratsa jihohin kudancin ƙasar aƙalla tara”, kamar yadda Bayo Onanuga ya bayyana.

Haka kuma sanarwar ta ce shugaban ƙasar zai ƙaddamar da aikin sake gina tituna har 330 a duka faɗin ƙasar.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a ranar Talata shugaban ƙasar zai koma koma Abuja babban birnin ƙasar, inda a nan ma ya tsara ƙaddamar da ayyuka ciki har da fara jigilar jirgin ƙasan fasinja da zai riƙa zagaya birnin Abuja.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp