fidelitybank

Tinubu zai halarci taron kasashen Larabawa da Afrika

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu zai halarci taron ƙasashen Larabawa da Afirka da za a yi a birnin Riyadh na ƙasar Saudiyya, a wani ɓangare na ƙoƙarin da gwamnatin kasar ke yi na jawo hannun jarin kasashen waje ga tattalin arzikin ƙasar.

Mashawarcin shugaban ƙasa na musamman kan harkokin yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Ajuri Ngelale ne ya bayyana hakan a ranar Lahadin da ta gabata yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban ƙasa a Abuja.

“Shugaban zai yi amfani da taron ne wajen jawo hannun jarin kasashen waje kai tsaye zuwa cikin kasar. Taron tabbas zai samar da fa’ida ta fuskar tattalin arzikin ƙasar da Afirka.”

Taron dai na ƙoƙarin zaƙulo fannonin haɗin gwiwa, da samar da ra’ayi bai daya ta fannin ilmi da gogewa, da zayyana ayyuka da tsare-tsare na kyautata alaƙa tsakanin kasashen Larabawa da Afirka.

Taron kuma ya mayar da hankali ne kan tunkarar kalubalen da duniya ke fuskanta, kamar tashe-tashen hankula da yaƙi da ta’addanci da fatara da ilimi da kiwon lafiya da samar da abinci da bashi da kuma sauyin yanayi.

An gudanar da taron na karshe ne a shekarar 2016. Ngelale ya ce, za a yi cikakken bayani kan tarurrukan da shugaban kasar zai yi da masu zuba jari, waɗanda suka shafi farfado da tattalin arzikin kasar.

Shugaba Tinubu dai zai samu rakiyar ‘yan majalisar ministoci da shugabannin ‘yan kasuwa, inda ake sa ran yin cikakken bayani a yayin ganawarsa da masu son zuba jari.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp