fidelitybank

Tinubu zai gana da zababbun ‘yan majalisa

Date:

Jam’iyyar APC mai mulki ta gayyaci zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, tare da mataimakinsa Kashim Shettima, da sauran zaɓaɓɓun sanatoci na ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar zuwa wata ganawa ta musamman.

An tsara gudanar da ganawar ranar Litinin a fadar gwamnati da ke Abuja babban birnin ƙasar.

Rahotonni na cewa an tsara ganawar ne domin tattauna batun shugabancin majalisun dokokin ƙasar biyu da yadda za a rarraba muƙaman majalisun zuwa shiyyoyin ƙasar daban-daban.

Karanta Wannan: Tinubu zai yi mulki har zuwa 2031 sannan Arewa ta yi mulki zuwa 2039 – Joe

Gayyatar ganawa da zaɓaɓɓun wakilan – wadda sakataren jam’iyyar na ƙasa, Iyiola Omisore ya sanya wa hannu aka kuma wallafa a shafin jam’iyyar na Twitter – ta bayyan cewa za a yi ganawar ne ranar Litinin 13 ga watan Maris da misalin ƙarfe 12:00 na rana.

Jam’iyyar ta kuma buƙaci duka zaɓaɓɓun wakilan su hallara tare da takardun shaidar cin zaɓe da hukumar zaɓen ƙasar ta ba su.

Ganawar na zuwa ne bayan da tuni wasu ‘yan majalisun suka fara bayyana sha’awarsu ta zama shugabannin majalisun dokokin ƙasar biyu.

Samun haɗin kan shugabancin majalisun biyu dai na da matuƙar tasiri wajen gudanar da ayyuka a ɓangaren shugaban ƙasa.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp