Wani dan majalisar wakilai na jam’iyyar PDP, Dan Amos, ya tabbatar da cewa akwai fata a karkashin gwamnatin Tinubu.
Dan majalisar ya ce wasu daga cikin matakan da gwamnati mai ci ta riga ta dauka na nuni da cewa Tinubu zai kara daukaka Najeriya.
Amos, wanda ke wakiltar mazabar Jema’a/Sanga ta Jihar Kaduna a Majalisar Dokoki ta kasa, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su marawa Shugaba Tinubu baya a yunkurinsa na ganin Nijeriya ta sake zama babbar kasa.
“Akwai fatan alheri ga al’ummarmu a karkashin Shugaba Tinubu, shugaban kasa ya zauna lafiya. Najeriya za ta sake zama mai girma,” Amos ya ce a wajen wani taro da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP daga mazabarsa a Kafanchan.
Ya kara da cewa akwai fatan Tinubu zai zama shugaban kowa.
Ya yi nuni da cewa talakawan Kudancin Kaduna na godiya ga shugaban kasa domin ya ba su hafsan soja na daya a kasar nan.
“Shugaban hafsan tsaron yana daya daga cikinmu kuma hakan ya nuna cewa shugaban kasa yana da alheri ga mutanen Kudancin Kaduna,” in ji shi.