fidelitybank

Tinubu zai farfaɗo da zaman lafiya a Filato – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bada tabbacin gwamnatin shugaba Bola Tinubu za ta maido da zaman lafiya a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato cikin kankanin lokaci.

Shettima ya ba da wannan tabbacin ne a ranar Juma’a a lokacin da ya ke karbar bakoncin wani basaraken gargajiya daga Mangu, Mishkahan Mwaghavul, John Hirse, wanda ya jagoranci tawagarsa a ziyarar ban girma zuwa ofishinsa da ke fadar shugaban kasa, Abuja.

A cewarsa, kowane bangare na Najeriya za a ji irin tasirin da gwamnati ke yi a gwamnatin shugaba Tinubu.

Shettima ya ce rikicin da ke faruwa a Filato ba shi da alaka da addini, yana mai jaddada cewa “ya zama wajibi mu fahimci kanmu mu zauna lafiya da juna.”

“Plateau kasa ce mai albarka da Musulmi da Kirista. Abin da ya haɗa mu tare ya wuce abin da ya raba mu.

“Wannan gwamnatin za ta yi amfani da duk wani abu da zai taimaka wajen magance duk wani sabani na siyasa a kokarin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

“Da yardar Allah za mu magance duk wani sabani na cikin gida da ma’anar siyasa da ma kabilanci da ke cikin rikicin da kuma tabbatar da samun mafita mai dorewa,” inji shi.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp