fidelitybank

Tinubu zai farfaɗo da zaman lafiya a Filato – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bada tabbacin gwamnatin shugaba Bola Tinubu za ta maido da zaman lafiya a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato cikin kankanin lokaci.

Shettima ya ba da wannan tabbacin ne a ranar Juma’a a lokacin da ya ke karbar bakoncin wani basaraken gargajiya daga Mangu, Mishkahan Mwaghavul, John Hirse, wanda ya jagoranci tawagarsa a ziyarar ban girma zuwa ofishinsa da ke fadar shugaban kasa, Abuja.

A cewarsa, kowane bangare na Najeriya za a ji irin tasirin da gwamnati ke yi a gwamnatin shugaba Tinubu.

Shettima ya ce rikicin da ke faruwa a Filato ba shi da alaka da addini, yana mai jaddada cewa “ya zama wajibi mu fahimci kanmu mu zauna lafiya da juna.”

“Plateau kasa ce mai albarka da Musulmi da Kirista. Abin da ya haɗa mu tare ya wuce abin da ya raba mu.

“Wannan gwamnatin za ta yi amfani da duk wani abu da zai taimaka wajen magance duk wani sabani na siyasa a kokarin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

“Da yardar Allah za mu magance duk wani sabani na cikin gida da ma’anar siyasa da ma kabilanci da ke cikin rikicin da kuma tabbatar da samun mafita mai dorewa,” inji shi.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp