Shugaba Bola Tinubu zai tafi Tanzania a yau Lahadi domin halartar taron ƙoli na Afirka kan makamashi a babban birnin ƙasar, Dar es Salaam, wanda za a fara gobe Litinin zuwa jibi Talata.
Taron wanda gwamnatin ƙasar ta Tanzania za ta karɓi baƙuncinsa da haɗin gwiwar Bankin Raya Afirka da kuma Bankin Duniya, zai kasance ne da nufin tabbatar da shirin samar da wutar lantarki ga mutum miliyan 300 a Afirka nan da shekara ta 2030 – shirin da ake yi wa laƙabi da ‘‘Mission 300.’’
A yayin taron shugabannin Afirka, da shugabannin harkokin kasuwanci a nahiyar da kungiyoyin farar hula za su yi ƙoƙarin samo dabarun ciyar da shirin gaba cikin hanzari.
Haka kuma taron zai yi musayar dabaru kan yadda za a shawo kan matsalar makamashi a nahiyar.
Mahalatta taron za su tattauna kan yadda za a samar da makamashi kan yankunan da suke da matsala cikin sauri da samar da makamashi maras gurɓata muhalli da ƙoƙarin shigar da ‘yankasuwa cikin harkar samar da makamashin.
A ranar farko ta taron ministocin makamashi na ƙasashen da ke halartar taron za su tattauna, yayin da a rana ta biyu shugabannin ƙasashen su kuma za su rattaɓa hannu kan daftarin shirin samar da makamashin na Afirka.