fidelitybank

Tinubu zai dawo Najeriya ranar Talata

Date:

Shugaba Bola Tinubu zai tafi Tanzania a yau Lahadi domin halartar taron ƙoli na Afirka kan makamashi a babban birnin ƙasar, Dar es Salaam, wanda za a fara gobe Litinin zuwa jibi Talata.

Taron wanda gwamnatin ƙasar ta Tanzania za ta karɓi baƙuncinsa da haɗin gwiwar Bankin Raya Afirka da kuma Bankin Duniya, zai kasance ne da nufin tabbatar da shirin samar da wutar lantarki ga mutum miliyan 300 a Afirka nan da shekara ta 2030 – shirin da ake yi wa laƙabi da ‘‘Mission 300.’’

A yayin taron shugabannin Afirka, da shugabannin harkokin kasuwanci a nahiyar da kungiyoyin farar hula za su yi ƙoƙarin samo dabarun ciyar da shirin gaba cikin hanzari.

Haka kuma taron zai yi musayar dabaru kan yadda za a shawo kan matsalar makamashi a nahiyar.

Mahalatta taron za su tattauna kan yadda za a samar da makamashi kan yankunan da suke da matsala cikin sauri da samar da makamashi maras gurɓata muhalli da ƙoƙarin shigar da ‘yankasuwa cikin harkar samar da makamashin.

A ranar farko ta taron ministocin makamashi na ƙasashen da ke halartar taron za su tattauna, yayin da a rana ta biyu shugabannin ƙasashen su kuma za su rattaɓa hannu kan daftarin shirin samar da makamashin na Afirka.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp