Fadar shugaban kasa, ta ce shugaban ƙasar, Bola Tinubu zai koma gida yau bayan kwashe kusan mako uku ba ya ƙasar.
Mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.
Sanarwar ta ce “Shugaba Tinubu zai dawo yau”.
A ranar 2 ga watan Afurilu ne Tinubu ya fice daga Najeriya zuwa Faransa, a wata ziyarar aiki, kamar yadda sanarwar da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta bayyana.
Sai dai bayan tafiyar Tinubu abubuwa da dama sun faru a ƙasar waɗanda suka janyo kiraye-kirayen komawar sa.
Hare-hare da aka kai a jihar Filato ta arewa maso tsakiyar ƙasar sun yi sanadiyyar kisan sama da mutum 100, baya ga wanda aka kai cikin makon da ya gabata a jihar Benue wanda shi ma ya kashe sama da mutum 50.
Haka nan wata nakiya da ta fashe kan hanyar Damboa zuwa Maiduguri ta hallaka aƙalla mutum takwas a jihar Borno, bayan gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya koka da ƙaruwar ayyukan ƙungiyar Boko Haram, wadda ya yi zargin tana karɓe iko wasu yankuna na jihar.
Jagororin adawar siyasar ƙasar, kamar Atiku Abubakar da Peter Obi duk sun soki kasancewar Tinubu a wata ƙasa yayin da Najeriya ke cikin hali na rashin tsaro.