fidelitybank

Tinubu zai dawo Najeriya bayan ziyara da ya yi

Date:

Fadar shugaban kasa, ta ce shugaban ƙasar, Bola Tinubu zai koma gida yau bayan kwashe kusan mako uku ba ya ƙasar.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Sanarwar ta ce “Shugaba Tinubu zai dawo yau”.

A ranar 2 ga watan Afurilu ne Tinubu ya fice daga Najeriya zuwa Faransa, a wata ziyarar aiki, kamar yadda sanarwar da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta bayyana.

Sai dai bayan tafiyar Tinubu abubuwa da dama sun faru a ƙasar waɗanda suka janyo kiraye-kirayen komawar sa.

Hare-hare da aka kai a jihar Filato ta arewa maso tsakiyar ƙasar sun yi sanadiyyar kisan sama da mutum 100, baya ga wanda aka kai cikin makon da ya gabata a jihar Benue wanda shi ma ya kashe sama da mutum 50.

Haka nan wata nakiya da ta fashe kan hanyar Damboa zuwa Maiduguri ta hallaka aƙalla mutum takwas a jihar Borno, bayan gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya koka da ƙaruwar ayyukan ƙungiyar Boko Haram, wadda ya yi zargin tana karɓe iko wasu yankuna na jihar.

Jagororin adawar siyasar ƙasar, kamar Atiku Abubakar da Peter Obi duk sun soki kasancewar Tinubu a wata ƙasa yayin da Najeriya ke cikin hali na rashin tsaro.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp