Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sallami ministoci biyar tare da naɗa wasu sababbi bakwai da kuma sauya wa goma ma’aikatu.
Wata sanarwa da fadar gwamnatin kasar ta fitar a shafinta na X, ta nuna cewa ministocin da aka cire su ne;
Waɗanda aka sallama:
1-Barr. Uju-Ken Ohanenye; ma’aikatar harkokin mata
2- Lola Ade-John; ministan harkokin yawon buɗe idanu
3- Farfesa Tahir Mamman; ministan ilimi
4- Abdullahi Muhammad Gwarzo; ƙaramin ministan gidaje da raya birane
5- Dr. Jamila Bio Ibrahim; ministar matasa
Waɗanda aka sauya wa ma’aikatu:
1-Hon Dr. Yusuf Tanko Sununu; ƙaramin ministan ilimi ya koma ƙaramin ministan jinƙai da rage talauci
2- Dr. Morufu Olatunji Alausa; ƙaramin ministan lafiya, ya koma ministan ilimi
3- Barr. Bello Muhammad Goronyo, ƙaramin ministan ruwa da tsafta, ya zama ministan ayyuka
4-Hon. Abubakar Eshiokpekha Momoh