A yayin da ake ci gaba da takun-saka a kan shugabancin majalisar wakilai ta 10, zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi watsi da yiwuwar sake maimaita maganar majalisar ta 8 a lokacin da ‘yan adawa suka fi karfin jam’iyyar All Progressives Congress (APC), kan shugabancin majalisar dokokin kasa.
Tinubu, wanda mataimakin shugaban jam’iyyar APC na Kudu maso Yamma, Isaac Kekemeke, ya wakilta, ya bayyana hakan a yayin taron lacca da aka shirya domin karrama shugaban kungiyar ta Afenifere, Cif Reuben Fasoranti, wanda ya cika shekaru 97 a karshen mako.
A cewarsa, har yanzu jam’iyyar na da isasshen lokacin da za ta hada bangarorin da ke rikici da juna kafin kaddamar da majalisar dokokin kasar.
Ya kawar da fargabar cewa ‘yan adawa za su yi awon gaba da shugabancin majalisar dokokin kasar.
“Yan adawa ba za su mamaye Majalisar Dokoki ta kasa ba; Shugaban kasa da jam’iyya mai jiran gado suna aiki tukuru don ganin cewa duk abin da kuka ga a matsayin fushi za a warware shi, kuma wannan dimokuradiyya ce,” inji shi.
A makon da ya gabata ne jam’iyyar APC ta amince da Sanata Godwill Akpabio da Tajudeen Abbas a matsayin shugaban majalisar dattawa kuma kakakin majalisar wakilai.
Tun a wancan lokaci masu neman shugabancin NASS na 10 suka yi barazanar kauracewa jam’iyyar.
A shekarar 2015, Bukola Saraki da Hon Yakubu Dogara sun yi nasarar lashe zaben shugabancin majalisar dokokin kasar ba tare da bukatar jam’iyyar APC mai mulki ba.