fidelitybank

Tinubu ya ya taya Laberiya murnar samun sabon shugaba

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya gwamnati da al’umar Laberiya murna kan samun nasarar kammala zaɓen shugaban ƙasar cikin kwanciyar hankali.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale, ya fitar, shugaba Tinubu ya taya sabon zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Joseph Boakai,murnar lashe zaɓen, tare da yin kira a gare shi da ya haɗa kan ‘yan ƙasar wajen gudanar mulki don samar wa ƙasar ci gaba.

Haka kuma shugaban na Najeriya ya jinjina wa shugaban Laberiya, George Weah, bisa nuna abinda ya kira “tattakun shugabanci da ba kasafai ake nuna irinsa ba” ta hanyar karɓar faɗuwa domin kauce wa rikici a ƙasar.

“Abin da shugaba Weah ya yi babban abin misali ne a tsarin dimokradiyya a wannan lokaci musamman a yankin Afirka ta Yamma, inda dimokradiyya ke fuskantar barazanar masu ƙwace wa mutane abin da suka zaɓa”, in ji Tinubu

“Haƙiƙa na jinjina wa shugaba George Weah bisa halin kima da dattaku da ya nuna. Ya nuna cewa bai kamata sakamakon zaɓen ya zama silar tashin hargitsi a ƙasar ba,” in ji shugaban na Najeriya.

Yarda da faɗuwa tare da taya abokin hamayya murnar lashe zaɓe, ba abu ne da aka saba gani ba a nahiyar Afirka, inda galibi waɗanda suka sha kaye kan garzaya kotu don neman haƙƙinsu, bisa zargin aikata maguɗi a zaɓukan da suka sha kayen.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp