Karamin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya umurci sojojin Najeriya da su tabbatar an kawo karshen ayyukan ta’addanci a 2025.
Matawalle ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da yake jawabi ga mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a gidansa da ke Gusau, inda ya tabbatar da cewa sojoji za su yi duk abin da ya dace domin bin umarnin shugaban kasa.
Da yake magana, tsohon gwamnan jihar Zamfara, ya ce gwamnatin tarayya ta kammala dukkan shirye-shiryen tura karin sojoji da kayan aikin soji zuwa yankunan da ake fama da rikici a shiyyar Arewa maso Yamma.
“Gwamnatin tarayya da shugabannin sojoji sun damu matuka game da batun masu ba da labari na taimaka wa ‘yan fashin.
“Wannan shine babban kalubalen rashin cin nasara a yakin da ake yi da ‘yan bindiga,” in ji shi.
Matawalle ya koka da yadda masu ba da labarin ’yan uwa ne da ke sayar da lamirinsu ga shaidan don neman kudi.
Hakazalika, ministan ya gargadi ‘yan siyasa da su daina cakude siyasa da batun tsaro.