fidelitybank

Tinubu ya umarci da a gaggauta binciken mutuwar Yara ƴan Islamiyya a Oyo

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya ba da umarnin a gaggauta gudanar da bincike domin musabbabin turmutsutsun da ya auku a jihar Oyo, wanda ya yi sanadiyar mutuwar yara da 35 da jikkata wasu a wurin taron al’ada na ya yara.

Tinubu ya bayyana wannan buƙatar ce a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar.

Shugaba Tinubu ya bayyana matuƙar kaɗuwarsa, sannan ya miƙa ta’aziyyarsa ga gwamanti da iyalan waɗanda abin ya shafa, da al’ummar jihar baki ɗaya.

“Kula da yaranmu nauyi ne da bai kamata a yi wasa da shi ba,” in ji shi, sannan ya ƙara da kira ga masu shirya taruka da su riƙa kula hanyoyin gudanar da tarukansu cikin tsanaki.

A ranar Alhamis, ƴansanda sun ce sun kama mutum bakwai da suka da alaƙa da shirya taron da ya janyo turmutsutsun, ciki har da wadda ta shirya taron, tsohuwar matar Ooni na Ife Naomi Silekunola.

Wasu iyayen da suka zanta da ƴanjarida sun ce sun raka yaransu taron ne domin an yi alƙawarin za a raba kuɗi naira 5,000 ga duk wanda ya je, sannan za a raba abinci kyauta.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp