fidelitybank

Tuntubi ya taya zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Ghana murnar lashe zaɓe

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya taya zababben shugaban kasa John Dramani Mahama murnar nasarar da ya samu a babban zaben kasar Ghana da aka gudanar ranar Asabar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

A cewar sanarwar, Tinubu a wata tattaunawa da ya yi da Mahama ta wayar tarho, ya bayyana fatan cewa hawan sa kan karagar mulki a karo na biyu zai kara kawo zaman lafiya a kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika, ECOWAS.

Tinubu ya yabawa al’ummar Ghana bisa jajircewarsu na tabbatar da dimokradiyya.

A cewarsa, an nuna hakan ne ta hanyar gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokoki cikin lumana da nasara.

Tinubu ya yabawa ‘yan Ghana bisa sake nuna wa duniya cewa dimokuradiyya ita ce hanyar da aka fi so wajen samun kwanciyar hankali a siyasance, ci gaban tattalin arziki, adalcin zamantakewa da gudanar da mulki cikin gaskiya a Afirka.

Ya tabbatar da cewa amincewar Najeriya da yankinsu kan ka’idojin ‘yancin jama’a na zaben shugabanninsu cikin ’yanci zai kasance abin alfahari.

Shugaban na Najeriya ya yabawa Dr Mahamudu Bawumia, dan takarar jam’iyyar New Patriotic Party (NPP) da mataimakin shugaban kasar Ghana, bisa amincewa da shan kaye kafin hukumar zaben Ghana ta bayyana a hukumance.

Tinubu ya ce matsayin Bawumia ya karfafa tsarin dimokradiyyar Ghana.

Ya ce komawar Mahama gidan Jubilee, bayan da ya rike mukamin shugaban kasa daga shekarar 2012 zuwa 2017, ya nuna amincewar al’ummar Ghana ga shugabancinsa da kuma hangen nesansa na kai kasar ga wani matsayi mai girma.

DAILY POST ta ruwaito cewa Mahama ya taba rike mukamin mataimakin shugaban kasar Ghana daga shekarar 2009 zuwa 2012, dan majalisar wakilai daga 1997 zuwa 2009, ya kuma rike mukamai na mataimakinsa da minista tsakanin 1998 zuwa 2001.

“Shugaba Tinubu ya sake sabunta cikakken goyon bayansa na zurfafa dankon zumunci tsakanin Najeriya da Ghana wanda tarihi ya gindaya, alakar al’adu, goyon bayan juna da hadin gwiwa, manufofin kasashen Afirka, dimokuradiyya, bin doka da oda da kuma hadewar tattalin arziki.

“Shugaban Najeriya ya gode wa shugaba Nana Akufo-Addo saboda kyakkyawan jagoranci da kuma gudummawar da ya bayar ga ci gaban Ghana da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Sanarwar ta ce “Shugaban yana fatan yin aiki tare da gwamnatin shugaba Mahama mai jiran gado don karfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu a bangarori daban-daban da kuma samar da makoma mai haske a yankin yammacin Afirka.”

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp