Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya taya zababben shugaban kasa John Dramani Mahama murnar nasarar da ya samu a babban zaben kasar Ghana da aka gudanar ranar Asabar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Lahadi a Abuja.
A cewar sanarwar, Tinubu a wata tattaunawa da ya yi da Mahama ta wayar tarho, ya bayyana fatan cewa hawan sa kan karagar mulki a karo na biyu zai kara kawo zaman lafiya a kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika, ECOWAS.
Tinubu ya yabawa al’ummar Ghana bisa jajircewarsu na tabbatar da dimokradiyya.
A cewarsa, an nuna hakan ne ta hanyar gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokoki cikin lumana da nasara.
Tinubu ya yabawa ‘yan Ghana bisa sake nuna wa duniya cewa dimokuradiyya ita ce hanyar da aka fi so wajen samun kwanciyar hankali a siyasance, ci gaban tattalin arziki, adalcin zamantakewa da gudanar da mulki cikin gaskiya a Afirka.
Ya tabbatar da cewa amincewar Najeriya da yankinsu kan ka’idojin ‘yancin jama’a na zaben shugabanninsu cikin ’yanci zai kasance abin alfahari.
Shugaban na Najeriya ya yabawa Dr Mahamudu Bawumia, dan takarar jam’iyyar New Patriotic Party (NPP) da mataimakin shugaban kasar Ghana, bisa amincewa da shan kaye kafin hukumar zaben Ghana ta bayyana a hukumance.
Tinubu ya ce matsayin Bawumia ya karfafa tsarin dimokradiyyar Ghana.
Ya ce komawar Mahama gidan Jubilee, bayan da ya rike mukamin shugaban kasa daga shekarar 2012 zuwa 2017, ya nuna amincewar al’ummar Ghana ga shugabancinsa da kuma hangen nesansa na kai kasar ga wani matsayi mai girma.
DAILY POST ta ruwaito cewa Mahama ya taba rike mukamin mataimakin shugaban kasar Ghana daga shekarar 2009 zuwa 2012, dan majalisar wakilai daga 1997 zuwa 2009, ya kuma rike mukamai na mataimakinsa da minista tsakanin 1998 zuwa 2001.
“Shugaba Tinubu ya sake sabunta cikakken goyon bayansa na zurfafa dankon zumunci tsakanin Najeriya da Ghana wanda tarihi ya gindaya, alakar al’adu, goyon bayan juna da hadin gwiwa, manufofin kasashen Afirka, dimokuradiyya, bin doka da oda da kuma hadewar tattalin arziki.
“Shugaban Najeriya ya gode wa shugaba Nana Akufo-Addo saboda kyakkyawan jagoranci da kuma gudummawar da ya bayar ga ci gaban Ghana da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
Sanarwar ta ce “Shugaban yana fatan yin aiki tare da gwamnatin shugaba Mahama mai jiran gado don karfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu a bangarori daban-daban da kuma samar da makoma mai haske a yankin yammacin Afirka.”