fidelitybank

Tinubu ya soke ayyukansa a Legas bisa mutanen da suka mutu a Abuja da Anambra

Date:

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya soke ayyukan da ya tafi yi a jiharsa ta Legas domin karrama wadanda suka mutu sakamakon turmutsutsin da ya janyo hasarar rayuka a Abuja da jihar Anambra.

Aƙalla mutum 10 sun mutu, ciki har da ƙananan yara, yayin da da dama suka samu raunuku sakamakon wani turmutsutsu da ya faru a cocin Catholic da ke unguwar Maitama a Abuja.

Cikin wata sanarwa da rundunar ‘yansandan birnin Abuja ta fitar, ta ce cikin waɗanda suka mutu har da ƙananan yara huɗu, yayin da mutum takwas suka samu munanan raunuka, kuma suke karɓar magani a asibiti.

Can ma a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin ƙasar rahotonni na cewa wasu mutane sun mutu bayan wani turmutsutsu da aka samu a wajen rabon tallafi a jihar a ranar ta Asabar.

Sanarwar da fadar shugaban Najeriyar ta fitar ta ce shugaban ya soke kallon wasan kwale-kwale da aka tsara zai yi a Ikoyi. Sannan ya yi wa mamatan addu’a tare da fatan murmurewa ga waɗanda suka jikkata.

Yan Najeriya na fama da matsin rayuwa sakamakon matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka kan tattalin arziki waɗanda suka kai ga janye tallafin man fetur wanda kuma ya haddasa tsadar kayan abinci da sufuri.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp