fidelitybank

Tinubu ya sauka a Saudiyya gabanin taron ƙasashe Musulmai

Date:

A ranar Lahadi ne shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya isa Riyadh babban birnin kasar Saudiyya domin halartar taron hadin gwiwa tsakanin kasashen Larabawa da Musulunci.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar.

Sanarwar ta ce, Tinubu ya sauka a filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz da karfe 10 na safe agogon kasar, kuma mataimakin gwamnan yankin Riyadh, Yarima Mohammed Bin Abdulrahman Bin Abdulaziz ya tarbe shi.

Taron wanda ke gudana bisa gayyatar Sarki Salman da Yarima mai jiran gado Mohammed Bin Salman, zai mayar da hankali ne kan halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya.

Tun da farko Onanuga ya ce taron zai tattauna wasu muhimman batutuwan yankin, musamman kan rikicin Isra’ila da Falasdinu.

A cewar Onanuga, Shugaban Najeriyar zai yi magana kan rikicin, inda ya jaddada matsayar Najeriya na tsagaita bude wuta cikin gaggawa da kuma bukatar gaggauta warware rikicin cikin lumana.

Ya kuma kara da cewa, Tinubu zai kuma matsa kaimi wajen ganin an sabunta yunkurin kasashen duniya na farfado da tsarin kasa biyu a matsayin hanyar da ta dace ta samar da zaman lafiya mai dorewa.

“A yayin taron, ana sa ran shugaba Tinubu zai yi jawabi kan rikicin Isra’ila da Falasdinu, yana mai jaddada kiran da Najeriya ta yi na tsagaita bude wuta cikin gaggawa da kuma bukatar a gaggauta warware rikicin cikin lumana.

“Najeriya kuma za ta ba da shawarar sake sabunta kokarin sake farfado da tsarin kasa biyu a matsayin hanyar samar da zaman lafiya mai dorewa a yankin,” in ji Onanuga.

Za a fara taron ne a ranar Litinin 11 ga Nuwamba, 2024.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...
X whatsapp