A ranar Lahadi ne shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya isa Riyadh babban birnin kasar Saudiyya domin halartar taron hadin gwiwa tsakanin kasashen Larabawa da Musulunci.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar.
Sanarwar ta ce, Tinubu ya sauka a filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz da karfe 10 na safe agogon kasar, kuma mataimakin gwamnan yankin Riyadh, Yarima Mohammed Bin Abdulrahman Bin Abdulaziz ya tarbe shi.
Taron wanda ke gudana bisa gayyatar Sarki Salman da Yarima mai jiran gado Mohammed Bin Salman, zai mayar da hankali ne kan halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya.
Tun da farko Onanuga ya ce taron zai tattauna wasu muhimman batutuwan yankin, musamman kan rikicin Isra’ila da Falasdinu.
A cewar Onanuga, Shugaban Najeriyar zai yi magana kan rikicin, inda ya jaddada matsayar Najeriya na tsagaita bude wuta cikin gaggawa da kuma bukatar gaggauta warware rikicin cikin lumana.
Ya kuma kara da cewa, Tinubu zai kuma matsa kaimi wajen ganin an sabunta yunkurin kasashen duniya na farfado da tsarin kasa biyu a matsayin hanyar da ta dace ta samar da zaman lafiya mai dorewa.
“A yayin taron, ana sa ran shugaba Tinubu zai yi jawabi kan rikicin Isra’ila da Falasdinu, yana mai jaddada kiran da Najeriya ta yi na tsagaita bude wuta cikin gaggawa da kuma bukatar a gaggauta warware rikicin cikin lumana.
“Najeriya kuma za ta ba da shawarar sake sabunta kokarin sake farfado da tsarin kasa biyu a matsayin hanyar samar da zaman lafiya mai dorewa a yankin,” in ji Onanuga.
Za a fara taron ne a ranar Litinin 11 ga Nuwamba, 2024.