fidelitybank

Tinubu ya sauka a Anambra ziyarar aiki

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya isa Awka, babban birnin jihar Anambra, a wata ziyarar aiki da ya kai jihar.

Da misalin karfe 12:15 na dare shugaban ya isa filin jirgin sama na Chinua Achebe dake Anambra, Gwamna Chukwuma Soludo ya tarbe shi.

Tinubu, yayin ziyarar zai kaddamar da gidan gwamnatin jihar Anambra a karon farko a ranar Alhamis, wanda ke nuna wani muhimmin tarihi fiye da shekaru 30 da samar da jihar.

Shugaban kasar zai kuma kaddamar da wasu ayyuka da dama da gwamnatin Gwamna Chukwuma Soludo ta aiwatar.

Kwamishinan Ayyuka na Jihar Anambra, Ifeanyi Okoma, a lokacin da yake magana a gidan Talabijin na Channels Television’s Sunrise Daily a ranar Alhamis, ya ce jama’ar jihar sun cika da murna da sabon gidan gwamnati da Soludo ya gina.

“Shekaru 34 a jihar Anambra ce kadai jihar da ba ta da gidan gwamnati kuma muna zaune a wani gida na wucin gadi da ke wajen babban birnin jihar da ke Amawbia.

“Amma a yau, akwai abin da za a yi murna, Jihar Anambra da yardar Allah ta hannun jagorancin Farfesa Charles Chukwuma Soludo, muna da gidan gwamnati da ke zaune kusa da hekta 8 na fili kuma zai kasance mafi girma kuma mafi korayen gidan jihar a kasar,” in ji Okoma.

Wannan dai shi ne karo na biyu da Tinubu ya kai ziyara yankin Kudu maso Gabas a bana, inda a baya ya ziyarci jihar Enugu a watan Janairu domin gudanar da wani taro na gari da masu ruwa da tsaki, da kuma ayyukan hukumar da suka hada da Magani Fun City.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...
X whatsapp