fidelitybank

Tinubu ya san jam’iyyar da na ke goyon baya – Sanusi

Date:

Yayin da zaben 2023 ke kara karatowa, tsohon Sarkin Kano, Sanusi Lamido Sanusi, ya bayyana jam’iyya daya tilo da ya ke goyon baya.

Sanusi ya ce jam’iyyar All Progressives Congress, APC, dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu na sane da cewa shi na jam’iyyar da ake kira Najeriya ne.

Ya bayyana hakan ne yayin da ya ke cewa shi ba dan kowace jam’iyya ba ne.

Sanusi ya yi wannan jawabi ne a lokacin da yake zantawa da Tinubu da sauran baki a Kaduna a yayin bikin KadInvest karo na bakwai, wanda hukumar bunkasa zuba jari ta jihar Kaduna ta shirya a jiya.

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN ya kuma koka da yadda ake satar mai, da karuwar basussukan da Najeriya ke fama da ita, rashin daidaiton biyan tallafin da ake samu da kuma hauhawar kudaden kasashen waje, da dai sauran kalubalen kudi da tattalin arziki da Najeriya ke fuskanta a halin yanzu.

Ya yi kira da a yi gaskiya da rikon amana wajen tafiyar da dukiyar kasa sannan kuma ya bukaci a kwancewa kamfanin man fetur na kasa (NNPC) Limited, yana mai cewa kamfanin ba saniya ba ce amma ya kamata a gudanar da shi a matsayin kamfani mai zaman kansa tare da bin diddigin al’amura.

Sanusi ya kuma bukaci Jihohin kasar da su ‘yantar da kansu daga dogaro da gwamnatin tarayya fiye da kima.

“Na ci gaba da maimaitawa, da fatan ku tuna cewa na rasa aiki a babban bankin kasa saboda wannan matsala.

“Ba batun wata jam’iyya ba ce. Bani da party. Jam’iyyata Najeriya ce. Wannan ita ce matsalar da muka samu a 2014. Asiwaju (Tinubu) ya san jam’iyyata ita ce Najeriya,” inji shi.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp