Yayin da zaben 2023 ke kara karatowa, tsohon Sarkin Kano, Sanusi Lamido Sanusi, ya bayyana jam’iyya daya tilo da ya ke goyon baya.
Sanusi ya ce jam’iyyar All Progressives Congress, APC, dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu na sane da cewa shi na jam’iyyar da ake kira Najeriya ne.
Ya bayyana hakan ne yayin da ya ke cewa shi ba dan kowace jam’iyya ba ne.
Sanusi ya yi wannan jawabi ne a lokacin da yake zantawa da Tinubu da sauran baki a Kaduna a yayin bikin KadInvest karo na bakwai, wanda hukumar bunkasa zuba jari ta jihar Kaduna ta shirya a jiya.
Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN ya kuma koka da yadda ake satar mai, da karuwar basussukan da Najeriya ke fama da ita, rashin daidaiton biyan tallafin da ake samu da kuma hauhawar kudaden kasashen waje, da dai sauran kalubalen kudi da tattalin arziki da Najeriya ke fuskanta a halin yanzu.
Ya yi kira da a yi gaskiya da rikon amana wajen tafiyar da dukiyar kasa sannan kuma ya bukaci a kwancewa kamfanin man fetur na kasa (NNPC) Limited, yana mai cewa kamfanin ba saniya ba ce amma ya kamata a gudanar da shi a matsayin kamfani mai zaman kansa tare da bin diddigin al’amura.
Sanusi ya kuma bukaci Jihohin kasar da su ‘yantar da kansu daga dogaro da gwamnatin tarayya fiye da kima.
“Na ci gaba da maimaitawa, da fatan ku tuna cewa na rasa aiki a babban bankin kasa saboda wannan matsala.
“Ba batun wata jam’iyya ba ce. Bani da party. Jam’iyyata Najeriya ce. Wannan ita ce matsalar da muka samu a 2014. Asiwaju (Tinubu) ya san jam’iyyata ita ce Najeriya,” inji shi.