fidelitybank

Tinubu ya samu nasara a kan Atiku da Obi

Date:

Kotun koli ta yi watsi da daukaka karar da Peter Obi na jam’iyyar Labour Party (LP) ya shigar bisa dalilansa na rashin cancantarsa.

A hukuncin daya yanke, kwamitin mutane bakwai na kotun ya tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa (PEPC) tare da tabbatar da zaben shugaban kasa Bola Tinubu.

Hukuncin da mai shari’a John Okoro ya yanke, wanda bai wuce mintuna biyar ba, ya ce akasarin batutuwan da ke cikin karar Obi sun warware ne a hukuncin da Atiku na PDP ya shigar a baya.

Mai shari’a Okoro ya ce batu daya tilo da ke cikin karar Obi wanda ba a cikin karar Atiku ba shi ne batun nadin mataimakin shugaban kasa Kashim Shettma.

Ya ce tun farko kotun koli ta warware batun da ya shafi Shettima na neman takara sau biyu a hukuncin da ta yanke ranar 9 ga watan Mayu a karar da PDP ta daukaka kan INEC da wasu mutane uku.

Mai shari’a Okoro ya ce bai kamata a sake gabatar da batun a gaban kotun koli ba daga wadanda suka shigar da kara wadanda tuni suka san hukuncin.

Haka kuma kotun ta yi fatali da Ĉ™arar Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp