Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya sa hannu kan dokar mafi ƙanƙantar albashi ta naira dubu 70,000.
Matakin ya kawo ƙarshen watannin da aka shafe ana tattaunawa tsakanin hukumomi da ƴan ƙwadago da kuma ɓangaren masu kamfanoni.
Tinubu ya sa hannu kan dokar a fadarsa da ke Abuja kwanaki bayan da majalisar dokokin ƙasar ta miƙa masa ƙudirin.
Matakin dai ya zo ne yayin da wasu al’ummar Najeriya ke shirin gudanar da zanga-zanga don nuna takaicinsu kan tsadar rayuwa da taɓarɓarewar tattalin arziki.