fidelitybank

Tinubu ya rantsar da sababbin Ministocin sa

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya rantsar da sababbin ministocin da ya naɗa a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan rantsar da su, Tinubu ya ce, “mun fara ƙoƙarin dawo da tattalin arzikinmu cikin hayyacinsa,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa, “muna kan tafarki mai kyau domin cika burinmu, ba ma don mu kaɗai ba, har da jin daɗin ƴaƴanmu da jikokinmu.”

Shugaban ƙasan ya ce duk da ƙalubalen da ake fuskanta, ana ci gaba da aikin inganta tattalin arzikin ƙasar.

Sai ya bayyana wa sababbin ministocin cewa an zaɓo su domin su bayar da gudunmuwarsu domin ceto ƙasar.

A ranar 23 ga Oktoba ce Tinubu na cire wasu ministoci guda biyar, sannan ya naɗa wasu guda bakwai.

A ranar 30 ga Oktoba kuma Majalisar Dattawa ta tantance tare da amincewa da sababbin ministocin wato: Ministan jinƙai da rage talauci Dr Nentawe Yilwatda da inistan ƙwadago, Muhammadu Maigari Dingyadi da ƙaramar ministar harkokin waje, Bianca Odumegwu-Ojukwu.

Sauran su ne; Ministan masana’antau da kasuwanci da zuba jari, Dr Jumoke Oduwole da ministan kula da dabbobi, Idi Mukhtar Maiha da ƙaramin minstan gidaje, Yusuf Abdullahi Ata da ƙaramar ministar ilimi, Dr Suwaiba Said Ahmad.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp