fidelitybank

Tinubu ya na tauye hakkin mutane da kungiyoyi – Atiku

Date:

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana matukar damuwarsa game da abin da ya kira a matsayin cin zarafin ƙungiyoyin fararen hula da masu fafutuka da kafafen yaɗa labarai a ƙarƙashin gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

A wata sanarwa da Atiku ya fitar a shafinsa na X, ya kwatanta irin yanayin da ake fama da shi a halin yanzu da mafi tsananin kwanaki na mulkin kama-karya na sojoji, yana mai nuna fargaba kan yadda gwamnati ke ƙara tauye haƙƙin jama’a da ƙara dabarunta na tsoratarwa.

Atiku ya ce “Kamen da aka yi wa shugaban NLC, Joe Ajaero misali ne ƙarara na kokarin da gwamnatin ke yi na rufe bakin ƙungiyoyin fararen hula da na ƙwadago.”

“Wannan matakin wani ɓangare ne na fafutukar da gwamnatin ke yi na tsoratar da manyan muryoyin jama’a a Najeriya.” in ji Atiku.

Atiku ya soki batun ƙaruwar barazanar ‘yancin ‘yan jarida.

Ya kuma bayyana matakin DSS na mamaye ofishin SERAP a matsayin cin zarafi ga kimar dimokraɗiyya.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi kira ga gwamnatin Tinubu da ta karkata akalarta daga murkushe ƙungiyoyin farar hula zuwa magance matsalar tsaro da ke addabar ƙasar.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp