fidelitybank

Tinubu ya na da nagartar shugabanci – Sanata Nnamani

Date:

Tsohon gwamnan jihar Enugu, Sanata Chimaroke Nnamani, ya yaba da yadda dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yake yi.

Sanatan na Gabashin Enugu ya c,e tsohon Gwamnan Legas ya inganta harkar lafiya sosai.

Nnamani, a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, ya ce abun yabo ne ga Tinubu cewa cutar kanjamau ta ragu a jihar Legas daga kashi 6.7 zuwa kashi 3.5 tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007 yayin da mata sama da 2,000 suka samu rigakafin kamuwa da cutar kanjamau daga uwa zuwa yara (PMTCT). a cibiyoyi 10 na PMTCT da aka kafa domin rigakafin cutar.

Ya tuna cewa Tinubu ya kaddamar da shirin yaki da cutar zazzabin cizon sauro inda sama da majiyyata miliyan 3.6 suka samu magani kyauta da kuma gidajen sauro sama da miliyan daya da kuma BCC/IEC da aka ba su.

Nnamani ya kara da cewa an samar da allurai sama da 181,627 na sinadarin Sulfadoxine-pyrimethamine, kuma an aiwatar da maganin rigakafin zazzabin cizon sauro na wucin gadi ga mata masu juna biyu.

“Don kawo karshen cutar shan inna, an kaddamar da shirin rigakafi na kasa, jihar Legas ta kasance mai mahimmanci kuma fiye da yara miliyan 2.5 sun karbi maganin,” in ji shi.

A karkashin gwamnatin Tinubu, ya ce, “Jihar Legas ta kaddamar da shirin kula da lafiya a makarantu, wanda ya samar da aikin tantance ido da kuma kula da lafiyar dalibai kusan 6,600 da kuma samar da madara kyauta ga makarantun gwamnati sama da 900 da adadinsu ya kai 297,000.

“Shirin Kiwon Lafiya da Haihuwa Kyauta na Tinubu, ya kara da cewa, ya shafi yara ‘yan kasa da shekaru 12 da manya sama da 60 kuma ba tare da tsadar kulawar haihuwa ga mata masu ciki ba.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp