fidelitybank

Tinubu ya na da nagartar shugabanci – Sanata Nnamani

Date:

Tsohon gwamnan jihar Enugu, Sanata Chimaroke Nnamani, ya yaba da yadda dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yake yi.

Sanatan na Gabashin Enugu ya c,e tsohon Gwamnan Legas ya inganta harkar lafiya sosai.

Nnamani, a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, ya ce abun yabo ne ga Tinubu cewa cutar kanjamau ta ragu a jihar Legas daga kashi 6.7 zuwa kashi 3.5 tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007 yayin da mata sama da 2,000 suka samu rigakafin kamuwa da cutar kanjamau daga uwa zuwa yara (PMTCT). a cibiyoyi 10 na PMTCT da aka kafa domin rigakafin cutar.

Ya tuna cewa Tinubu ya kaddamar da shirin yaki da cutar zazzabin cizon sauro inda sama da majiyyata miliyan 3.6 suka samu magani kyauta da kuma gidajen sauro sama da miliyan daya da kuma BCC/IEC da aka ba su.

Nnamani ya kara da cewa an samar da allurai sama da 181,627 na sinadarin Sulfadoxine-pyrimethamine, kuma an aiwatar da maganin rigakafin zazzabin cizon sauro na wucin gadi ga mata masu juna biyu.

“Don kawo karshen cutar shan inna, an kaddamar da shirin rigakafi na kasa, jihar Legas ta kasance mai mahimmanci kuma fiye da yara miliyan 2.5 sun karbi maganin,” in ji shi.

A karkashin gwamnatin Tinubu, ya ce, “Jihar Legas ta kaddamar da shirin kula da lafiya a makarantu, wanda ya samar da aikin tantance ido da kuma kula da lafiyar dalibai kusan 6,600 da kuma samar da madara kyauta ga makarantun gwamnati sama da 900 da adadinsu ya kai 297,000.

“Shirin Kiwon Lafiya da Haihuwa Kyauta na Tinubu, ya kara da cewa, ya shafi yara ‘yan kasa da shekaru 12 da manya sama da 60 kuma ba tare da tsadar kulawar haihuwa ga mata masu ciki ba.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban Ĉ™asar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta Ĉ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin Ĉ™asarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaĈ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga Ĉ™asar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa Ĉ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin Ĉ™asar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp