fidelitybank

Tinubu ya naɗa majalisar gudanarwar hukumar raya yankin Arewa maso Yamma

Date:

Shugaban kasa Bola Tinubu aike da sunayen shugabannin majalisar gudanarwar sabuwar hukumar raya yankin arewa maso yammacin ƙasa zuwa ga majalisar dattawan ƙasar domin amince wa naɗinsu.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar ya ce matakin na zuwa ne bayan sanya hannu kan dokar da ta amince da ƙirƙiro sabuwar hukumar.

A ranar 24 ga watan Yuli ne dai Shugaba Tinubu ya sanya hannu kan sabuwar dokar.

Mutanen da Shugaba Tinubun ya aike da sunayensu don jagorantar sabuwar hukumar sun haɗa da:

Ambassada Haruna Ginsau (Jigawa) a matsayin shugaban majalisar gudanarwar hukumar.

Farfesa Abdullahi Shehu Ma’aji (Kano) a matsayin shugaban hukumar.

Sauran mambobin hukumar sun haɗa da :

  • Dakta Yahaya Umar Namahe (Sokoto)
  • Hon. Aminu Suleiman (Kebbi)
  • Sen. Tijani Yahaya Kaura (Zamfara)
  • Hon. Abdulkadir S. Usman (Kaduna)
  • Hon. Engr. Muhammad Ali Wudil (Kano)
  • Shamsu Sule (Katsina)
  • Nasidi Ali (Jigawa)

Sanarwar ta ci gaba da cewa ana sa ran sabbin shugabannin za su yi amfani da ƙwarewarsu wajen gina sabuwar hukumar.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp