Shugaban kasa Bola Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan marigayi Sanata Ifeanyi Ubah.
Sanata Uba wanda ya wakilci mazabar Anambra ta Kudu a majalisar dattawan kasar ya rasu ne da safiyar Asabar.
Ya kasance shahararren dan kasuwa kuma dan takarar gwamna a zaben gwamnan jihar Anambra da ke tafe.
Da yake mayar da martani kan lamarin, shugaba Tinubu a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Cif Ajuri Ngelale ya fitar, ya yi addu’ar Allah ya kara wa iyalan mamacin karfin gwiwa.
“Shugaba Tinubu ya jajanta wa abokai da abokan aikin marigayi Sanata, Majalisar Dokoki ta kasa, da gwamnati da al’ummar Jihar Anambra kan wannan babban rashi.
“Shugaban ya yi addu’ar Allah ya hutar da ran dan majalisar da ya rasu, tare da baiwa iyalansa karfin gwiwa da ta’aziyya,” in ji shi.