fidelitybank

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa bisa rasuwar mai ɗakin cif MKO Abiola, Dr Doyinsola Hamidat Abiola wadda ƴar jarida ce da ta yi fice.

Sanarwar da aka fitar daga Fadar Shugaban na Najeriya ta ambato irin gudummawar da Doyin Abiola wadda ta rasu tana da shekara 82 ta bayar a fannoni da dama musamman a ɓangaren jarida da kuma samar da daidaito tsakanin jinsi.

Sanarwar ta kuma yi magana kan rawar da ta taka wajen raya dimokraɗiyya inda ta yi riƙo da gaskiya da kuma ƙoƙarin samar da shugabanci na gari.

A cewar sanarwar, shugaban ya bayyana kyakkyawar alaƙar da ke tsakaninsa da marigayiyar wadda ta samo asali daga irin dangantaka ta ƙut da ƙut da ke tsakaninsa da marigayi MKO Abiola.

Ya ce ta bayar da gudummawa a zaɓen MKO inda bayan da aka soke zaɓen 12 ga watan Yuni da mai gidanta ya lashe, ta tashi tsaye wajen ganin an yi adalci.

Ya ƙara da cewa ƴan Najeriya ba za su mance da Doyin Abiola ba saboda ƙwarewarta a fannin jarida da kuma yadda take jagorantar tallafawa mata da kuma ƙoƙarin bayar da gudunmuwa a fannin dimokraɗiya.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...

Bajintar ɗaliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a ƙasa – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya ƴanmatan nan uku...

Ƙudirin faɗaɗa mamayar Gaza zai ƙara jefa Falasɗinawa cikin hatsari – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...
X whatsapp