Shugaba Bola Tinubu ya bayyana mutuwar Aderonke Kale, mace ta farko da ta fara kai wa mukamin Manjo Janar a rundunar sojin Najeriya, a matsayin asara mai zafi ga kasar.
Kale, wadda kuma ita ce mace da ta fara zama kwamandar rundunar sojoji likitoci, ta rasu ne ranar Alhamis tana da shekara 84.
A cikin wata sanarwa da fadar shugaban Najeriya ta fitar, Bola Tinubu ya mika sakon ta’aziyya ga ‘ya’ya da dangin Janar Kale mai ritaya da kuma rundunar sojin Najeriya da kungiyoyin likitoci na Najeriya kan rasuwar daya daga cikinsu.
Tinubu ya ce a matsayinta na mace ta farko a fagen da ta yi zarra, marigayiyar Manjo Janar din ”mai dumbin kwarin gwiwa da kwarewar aiki da kwazo da juriya irinta matan Najeriya”.
Shugaba Tinubu ya yi addu’ar neman jin kai ga marigayiyar, kuma ya yi fatan ‘yan’uwa da dangi za su yi hakuri kan wannan rashi da suka yi.