Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Neja, sakamakon rasuwar mutum 17 a hatsarin mota.
Hatsarin ya faru ne a ƙaramar hukumar Magama, inda ya ritsa da mutum 229 da ke cikin wata babbar mota.
Jami’in wayar da kai na hukumar kiyaye haɗurra, Bisi Kazeem, ya ce an yi nasarar ceto maza 206, da mace ɗaya, da ƙaramin yaro, waɗanda suka ji raunuka daban-daban.
Shugaba Tinubu ya kwatanta hatsarin da tsautsayi “kuma ya nemi hukumar ba da agaji ta tabbatar an bai wa waɗanda suka ji rauni kulawar da suke buƙata”, in ji wata sanarwa daga fadar shugaban.