fidelitybank

Tinubu ya mayarwa da Kwankwaso kakkausar martani

Date:

Musayar kalamai ta ɓarke tsakanin fadar shugaban, Bola Ahmed Tinubu da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamanan Kano, Sanata Rabi’u Musa kwankwaso kan zargin da Kwankwason ya yi na cewar gwamantin Bola Ahmed Tinubu na ƙoƙarin ƙaƙaba dokar ta ɓaci a jihar Kano.

Yayin wani taron ƙaddamar da aiki da gwamnatin jihar Kano ta gudanar, an jiyo Kwankwaso na zargin cewa “wasu sun haɗa baki da jagororin jam’iyyar APC suna ƙoƙarin fakewa da batun rikicin masarautar Kano su tayar da fitina, don gwamnatin tarayya ta samu damar ƙaƙaba dokar ta ɓaci”.

Sai dai Fadar shugaban ƙasar ta yi watsi da zargin da Kwankwason ya yi, tana bayyana shi a matsayin marar tushe ballantana makama.

“Abun mamaki ne a ce mutum kamarsa ya fito ya yi irin waɗannan kalamai, musamman zargin da ya yi na cewar ana son a saka dokar ta ɓaci a Kano ko tayar da rikici a jihar, ko kaɗan babu ƙanshin gaskiya kan waɗannan zarge-zarge, kuma a matsayinmu na gwamnatin tarayya ba a taɓa yin makamanciyar wannan maganar ba”. Inji Abdul Aziz Abdul’aziz

Har Ila yau ya ƙara da cewa batun masarautar Kano al’amari ne da ke gaban kotu, kuma jami’an tsaro suna bin duk wani umarnin kotu don tsare hakkin kowanne ɓangare, inda ya ƙara da cewa shugaba Tinubu na da kusancin da dukkannin mutum biyun da ake taƙaddama a kansu.

“Shugaban ƙasa na da alaƙa me kyau da waɗannan mutane biyu da ake taƙaddama a kansu, ba zai yi wani abu da zai kawo cin zarafi ko ace a matsayinsa na shugaban ƙasa, da yake da alhakin kula da kare dukiya da rayukan ƴan Najeriya a ce gwamnatinsa ta yi wani abu irin wanda Rabi’u Kwankwason ya yi zargi ba, don haka mu a ganinmu ya yi kalaman ne don kawai a harzuƙa magoya baya kuma a yi siyasa” inji Abdulaziz

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp