fidelitybank

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game da zargin da ƴan adawar ƙasar ke wa jam’iyya mai mulki na cewa tana son mayar da ƙasar kan tsarin jam’iyya ɗaya.

Tinubu ya mayar da martanin ne a cikin jawabinsa na ranar dimokurɗiyyar ƙasar, yau Alhamis 12 ga watan Yunin 2025 a zauren majalisar dokokin ƙasar.

Ya ce: “Tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu. Kuma ba zai taɓa zama cikin manufofinmu ba.”

Sai dai shugaban ya ce wannan ba zai hana jam’iyyar APC yin maraba da duk wanda ke son shiga cikinta ba.

“Zai kasance mun yi maguɗin siyasa idan muka hana mutane daga wasu jam’iyyun siyasa shigowa jam’iyyar APC,” in ji Tinubu.

A baya-bayan nan jam’iyyar APC ta karɓi wasu daga cikin gwamnoni da sanatoci da kuma ƴan majalisar dokokin tarayya da suka sauya sheƙa zuwa cikinta daga jam’iyyun adawa.

Sai dai jam’iyyun adawar sun zargi APC da kuma shugaba Tinubu da shafa wa ƴan siyasar zuma a baki domin jan hankalinsu su koma cikin jam’iyyar mai mulki.

Tuni dai fagen siyasa na Najeriya ya ɗauki zafi duk kuwa da cewa a watan da ya gabata ne gwamnati mai ci ta ci rabin wa’adin shugabancinta na shekara huɗu.

A shekarar 2027 ne za a yi babban zaɓen ƙasar na gaba, inda ake sa ran Tinubu – wanda jam’iyyarsa ta APC ta ce shi ne “ɗan takararta ɗaya tilo” na shugaban ƙasa zai sake tsayawa takara.

Masu sharhi na ganin cewa mayar da hankali kan zaɓen na 2027 tun yanzu ba abu ne mai alfanu ga ƙasar ba, kasancewar shugabanni za su mayar da hankali kan siyasa a maimakon yin ayyukan ci gaban al’umma.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp