Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game da zargin da ƴan adawar ƙasar ke wa jam’iyya mai mulki na cewa tana son mayar da ƙasar kan tsarin jam’iyya ɗaya.
Tinubu ya mayar da martanin ne a cikin jawabinsa na ranar dimokurɗiyyar ƙasar, yau Alhamis 12 ga watan Yunin 2025 a zauren majalisar dokokin ƙasar.
Ya ce: “Tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu. Kuma ba zai taɓa zama cikin manufofinmu ba.”
Sai dai shugaban ya ce wannan ba zai hana jam’iyyar APC yin maraba da duk wanda ke son shiga cikinta ba.
“Zai kasance mun yi maguɗin siyasa idan muka hana mutane daga wasu jam’iyyun siyasa shigowa jam’iyyar APC,” in ji Tinubu.
A baya-bayan nan jam’iyyar APC ta karɓi wasu daga cikin gwamnoni da sanatoci da kuma ƴan majalisar dokokin tarayya da suka sauya sheƙa zuwa cikinta daga jam’iyyun adawa.
Sai dai jam’iyyun adawar sun zargi APC da kuma shugaba Tinubu da shafa wa ƴan siyasar zuma a baki domin jan hankalinsu su koma cikin jam’iyyar mai mulki.
Tuni dai fagen siyasa na Najeriya ya ɗauki zafi duk kuwa da cewa a watan da ya gabata ne gwamnati mai ci ta ci rabin wa’adin shugabancinta na shekara huɗu.
A shekarar 2027 ne za a yi babban zaɓen ƙasar na gaba, inda ake sa ran Tinubu – wanda jam’iyyarsa ta APC ta ce shi ne “ɗan takararta ɗaya tilo” na shugaban ƙasa zai sake tsayawa takara.
Masu sharhi na ganin cewa mayar da hankali kan zaɓen na 2027 tun yanzu ba abu ne mai alfanu ga ƙasar ba, kasancewar shugabanni za su mayar da hankali kan siyasa a maimakon yin ayyukan ci gaban al’umma.