fidelitybank

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game da zargin da ƴan adawar ƙasar ke wa jam’iyya mai mulki na cewa tana son mayar da ƙasar kan tsarin jam’iyya ɗaya.

Tinubu ya mayar da martanin ne a cikin jawabinsa na ranar dimokurɗiyyar ƙasar, yau Alhamis 12 ga watan Yunin 2025 a zauren majalisar dokokin ƙasar.

Ya ce: “Tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu. Kuma ba zai taɓa zama cikin manufofinmu ba.”

Sai dai shugaban ya ce wannan ba zai hana jam’iyyar APC yin maraba da duk wanda ke son shiga cikinta ba.

“Zai kasance mun yi maguɗin siyasa idan muka hana mutane daga wasu jam’iyyun siyasa shigowa jam’iyyar APC,” in ji Tinubu.

A baya-bayan nan jam’iyyar APC ta karɓi wasu daga cikin gwamnoni da sanatoci da kuma ƴan majalisar dokokin tarayya da suka sauya sheƙa zuwa cikinta daga jam’iyyun adawa.

Sai dai jam’iyyun adawar sun zargi APC da kuma shugaba Tinubu da shafa wa ƴan siyasar zuma a baki domin jan hankalinsu su koma cikin jam’iyyar mai mulki.

Tuni dai fagen siyasa na Najeriya ya ɗauki zafi duk kuwa da cewa a watan da ya gabata ne gwamnati mai ci ta ci rabin wa’adin shugabancinta na shekara huɗu.

A shekarar 2027 ne za a yi babban zaɓen ƙasar na gaba, inda ake sa ran Tinubu – wanda jam’iyyarsa ta APC ta ce shi ne “ɗan takararta ɗaya tilo” na shugaban ƙasa zai sake tsayawa takara.

Masu sharhi na ganin cewa mayar da hankali kan zaɓen na 2027 tun yanzu ba abu ne mai alfanu ga ƙasar ba, kasancewar shugabanni za su mayar da hankali kan siyasa a maimakon yin ayyukan ci gaban al’umma.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...
X whatsapp