fidelitybank

Tinubu ya karbi jakadun Masar da Girka

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya karbi wasikun jakadu daga kasashen Masar, Girka da Pakistan da aka aika zuwa kasar nan.

Tarbar ya baiwa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, damar sake tabbatar da dabarun da Najeriya ke da shi a Afirka, a matsayin tushen zaman lafiya, yana mai cewa al’ummar kasar nan za ta ci gaba da taka rawa a matsayin mai tabbatar da zaman lafiya a nahiyar.

Da farko da yake karbar takardar amincewa daga jakadan Masar a Najeriya, Mohamed Ahmed, ya ce, Tinubu ya jaddada aniyar kasashen biyu na inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya ta hanyar hadin gwiwa tsakanin kungiyoyin kasa da kasa, kamar Majalisar Dinkin Duniya.

Ya kuma bayyana cewa, tun bayan kulla huldar diflomasiyya a shekarar 1961, Najeriya da Masar sun hada kai kan muhimman abubuwan da kasashen duniya suka sa gaba, ciki har da samar da zaman lafiya da tsaro da kwanciyar hankali a yankin.

Tattaunawar da aka yi a taron ta kuma tabo halin da ake ciki a yankin Sahel da Sudan.

Da yake amincewa da rawar da Masar ke takawa wajen sasanta rikicin Gaza, Tinubu ya ce, A na bukatar samun zaman lafiya a yankin Gaza.

Ambasada Ahmed ya isar da aniyar shugaba Abdel Fattah el-Sisi na karfafa dangantakar tattalin arziki da Najeriya, yana mai jaddada aniyar kasar Masar na kara kasuwanci da zuba jari a tsakanin kasashen biyu.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp