Gabanin bikin rantsauwa a ranar Litinin, zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tarbi tsohon firaministan kasar Birtaniya, Tony Blair a gidan tsaro da ke Abuja ranar Talata.
Tinubu ya bayyana hakan ne ta shafin sa na Twitter.
A cewar shugaban mai jiran gado, ya yi tattaunawa mai ma’ana da Tony Blair kan batutuwan da suka dace.
“Na tarbi tsohon firaministan kasar Birtaniya kuma wanda ya kafa Tony Blair Institute for Good Governance, Mr Tony Blair, a gidan tsaro dake Abuja, a safiyar yau. Mun tattauna batutuwan da suka shafi moriyar juna da yadda Najeriya za ta ci gaba da cin gajiyar ayyukan ban mamaki na Cibiyar,” ya rubuta.
Kashim Shettima, mataimakin shugaban kasa mai jiran gado, da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, na daga cikin wadanda suka halarci ziyarar Blair.
Blair shine wanda ya kafa cibiyar Tony Blair don kyakkyawan shugabanci.
Za a gabatar da bikin rantsar da Tinubu a ranar 29 ga Mayu.
Shugaban Amurka Joe Biden ya bayyana jerin tawagar da za su halarci bikin a Abuja.