fidelitybank

Tinubu ya kamata ka yi wa ‘yan kasa bayani a kan bashin dala biliyan 3.3 – Atiku

Date:

Jagoran adawar hamayya, Atiku Abubakar, ya ce, ya kamata gwamnatin shugaba Tinubu ta fito ta yi wa ‘yan Najeriya bayani kan bashin dala biliyan 3.3 da kamfanin mai na ƙasar NNPC ta ciyo da nufin farfaɗo da darajar kudin ƙasar.

A shekarar da ta gabata ne Kamfanin mai na ƙasar NNPC ciyo bashin domin taimakawa wajen farfaɗo da darajar naira a kasuwar musayar kuɗaɗe.

To sai dai a cikin wata sanarwar da tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya fitar, ya ce wani abin mamaki shi ne har yanzu gwamnati ba ta ce komai ba game da lamarin, kuma bayanan kawai da ake samu kan batun, ana samun su ne ta wasu majiyoyin da ba na hukuma ba daga kamfanin.

”An ƙulla yarjejeniyar ce da nufin biyan kuɗin da man fetur, wanda aka ƙulla da bankin ”African Export-Import” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Atiku Abubakar ya ce abin da suka gano shi ne a yanzu Najeriya na haƙo gangar mai miliyan 1.38 a kowace rana, kuma daga cikin ƙa’idojin yarjejeniyar bashin akwai batun cewa Najeriya za ta riƙa bayar da ganga 90,000 a kowace rana da nufin biyan bashin, daga 2024 har zuwa ganga miliyan 164.25 da za a kammala biyan bashin da shi.

”To a nan ne matsalar take, domin kuwa abin da Najeriya ta tsara za ta riƙa sayar da kowace gangar mai a shekarar 2024 shi ne dala 77.96”, in ji Atiku.

”Ka ga idan aka lissafa wannan kuɗi da miliyan 164.25, kuɗin zai kama dala biliyan 12, a kan wannan ne muke son gwamnati ta fito ta yi mana bayanin yadda yarjejeniyar take”, in ji jagoran adawar ƙasar.

Sanarwar ta ce abu ne da hankali ba zai iya ɗauka ba, a ce gwamnatin tarayya za ta karɓo bashin dala biliyan 3.3 da kuɗin ruwa na kashi 12, amma ƙiyasin abin da za a biya a ce ya kai dala biliyan 12.

Wannan na nufin cewa an samu bambancin dala biliyan bakwai tsakanin abin da ke rubuce a takarda da abin da yake a zahiri.

Atiku Abubakar ya ce akwai tambayoyin da ‘yan ƙasar ke buƙatar sanin amsarsu game da yarjejeniyar, kan haka ne muke buƙatar gwamnatin tarayya ta fito ƙarara ta yi bayaninsu.

”Don haka muke kira a madadin ‘yan Najeriya, gwamnatin tarayya ta amsa mana waɗanna tambayoyi”.

1. Shin gwamnatin tarayya ce ta ƙarbo bashin?

2. Shin bashin na daga cikin basussukan da majalisa ta amince wa gwamnati?

3. Su wane ne a cikin yarjejeniyar bashin, kuma wace rawa za su taka a yarjejeniyar?

4. Waɗanne ne ƙa’idojin bashin, ciki har da wanda ya ciwo shi, da yadda za a biya, da kadarar da aka ajiye don ƙulla yarjejeniyar, da kuma kuɗin ruwa?

5. Daga ƙarshe, kuma me ya sa wani kamfanin Bahamas ke cikin yarjejeniyar?

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp