Shugaba Bola Tinubu, ya kafa kwamitin karta-kwana da zai samar da hanyoyin daidaita tattalin arzikin ƙasar da ke ci gaba da fuskantar tasku.
Farashin kayan abinci da mai ya yi tashin gwauron zabi kuma mutane da dama na fama kasancewar albashinsu bai wadatar ba wajen biyan buƙatunsu na yau da kullum ba.
Ƙalubalen tattalin arzikin ya janyo matsin rayuwa ga mutane da dama abin da kuma ke ƙara matsa lamba kan gwamnatin Tinubu.
Wasu na ganin janye tallafin mai da faɗuwar darajar naira ne suka janyo matsalolin.
Sai dai hukumomi sun ce yi wa tattalin arzikin ƙasar garambawul ya zama dole saboda makomar ƙasar.
Shugaban ya umarci kwamitin ya gabatar da cikakken tsarin farfaɗo da tattalin arziki cikin mako biyu wanda za a aiwatar cikin wata shida.
Manyan jami’an gwamnati da kuma ƴan kasuwa ne mambobin kwamitin.
Shugaban ya kuma kafa kwamitin shugaban ƙasa da zai kula da harkokin tattalin arziki, wanda kuma zai jagoranci sa ido kan sauye-sauyen tattalin arziki.