fidelitybank

Tinubu ya kaddamar da kwamitin warware matsalar tattalin arziki

Date:

Shugaba Bola Tinubu, ya kafa kwamitin karta-kwana da zai samar da hanyoyin daidaita tattalin arzikin ƙasar da ke ci gaba da fuskantar tasku.

Farashin kayan abinci da mai ya yi tashin gwauron zabi kuma mutane da dama na fama kasancewar albashinsu bai wadatar ba wajen biyan buƙatunsu na yau da kullum ba.

Ƙalubalen tattalin arzikin ya janyo matsin rayuwa ga mutane da dama abin da kuma ke ƙara matsa lamba kan gwamnatin Tinubu.

Wasu na ganin janye tallafin mai da faɗuwar darajar naira ne suka janyo matsalolin.

Sai dai hukumomi sun ce yi wa tattalin arzikin ƙasar garambawul ya zama dole saboda makomar ƙasar.

Shugaban ya umarci kwamitin ya gabatar da cikakken tsarin farfaɗo da tattalin arziki cikin mako biyu wanda za a aiwatar cikin wata shida.

Manyan jami’an gwamnati da kuma ƴan kasuwa ne mambobin kwamitin.

Shugaban ya kuma kafa kwamitin shugaban ƙasa da zai kula da harkokin tattalin arziki, wanda kuma zai jagoranci sa ido kan sauye-sauyen tattalin arziki.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp