Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shaidawa Bola Ahmed Tinubu, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC mai mulki, da ya hakura ya kula da lafiyarsa a maimakon neman takarar shugaban kasa a 2023 da yake yi.
Kalaman na Kwankwanso ya biyo bayan matakin da Tinubu ya dauka na sasantawa da tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima, a matsayin abokin takara.
Da yake magana kan lamarin a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a jiya, tsohon gwamnan na Kano ya ce, yakin neman zaben 2023 zai yi tsauri.
A cewarsa, jam’iyyar APC mai mulki ta gaza ta fuskoki da dama da kuma rasa kwarin gwiwar ‘yan Najeriya.
Ya ce: “Idan ka ga abokina Bola, ka gaya masa ya sauƙaƙa, ya kula da lafiyarsa sosai. Domin ina son shi sosai, shi abokina ne. Wannan yakin yana da matukar tsauri, yana bukatar kokari sosai da dai sauransu. Ina fatan zai yi sauki, domin mu ci gaba da fafutukar tabbatar da kasa daya mai karfi da wadata a Nijeriya.