fidelitybank

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan tawagar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasar 24 – Super Falcons – tukwicin kuɗi dala 100,000 kowanne, kimanin naira miliyan 153.

Haka nan ya bai wa kowa daga cikinsu kyautar gida mai ɗaki uku, yayin da ya bai wa tawagar masu horas da su kyautar dala 50,000.

Tinubu ya sanar da hakan ne a yau Litinin sa’ilin da ya tarbi tawagar matan bayan nasarar da suka samu ta lashe kofin ƙwallon ƙafa na Afirka karo na 10.

A ranar Asabar ne Super Falcons suka lallasa Atlas Lionesses na Morocco da ci uku da biyu a wasan ƙarshe na gasar cin kofin da Moroccon ta karbi baƙunci.

Baya ga kyautar kuɗi da gida, Tinubu ya kuma karrama ƴan wasan da lambar girmamawa ta ƙasa ta OON.

Haka nan kuma ƙungiyar gwamnonin Najeriya ta bai wa tawagar ta Super Falcons kyautar kudi naira miliyan 10.

A lokacin da yake jawabi, Tinubu ya ce: “Na karɓi wannan kofi a madadin ƴan Najeriya, kuma zan ce muku: mun gode da wannan ƙwazo, saboda haka na karrama ƴan wasan da masu horas da su 11 da lamabar girmamawa ta Officer of the Order of the Niger (OON).

“Bugu da ƙari na bayar da umarnin a bai wa dukkanin ƴan wasa da masu horas da su gidaje masu ɗakuna uku-uku.

“Haka nan kuma, akwai kyautar kudin naira kwatankwacin dala 100,000 ga kowace ƴar wasa 24 da kuma dala 50,000 ga tawagar masu horaswa.”

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘ƴan ƙungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...
X whatsapp