Shugaban kasa Bola Tinubu ya nada shugabannin hukumar da manyan jamiāan gudanarwa na hukumomin gwamnain tarayya guda 42 da kuma sakatare a hukumar tsaro ta farin kaya da shige da fice da kuma gidajen yari.
ciki wanda ya rabauta harda, Dr Abdullahi Umar Ganduje, shugaban jam’iyyar APC a matsayin shugaban hukumar kula da filayen jiragen sama na kasa da tashohin jiragen ruwa.
Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Jumaāa, ta ce Tinubu ya kuma nada sabon manajan darakta na kamfanin jiragen kasa na Najeriya da kuma babban darakta a hukumar kula da fasahar kere-kere ta kasa, NBTI.
A cewar sanarwar, Tinubu ya umurci wadanda aka nada āka da su tsoma baki a harkokin tafiyar da kungiyoyin,ā yana mai jaddada cewa matsayinsu ba na zartarwa ba ne.
Onanuga ya kara da cewa dukkan nade-naden na fara aiki nan take.