fidelitybank

Tinubu ya gargaɗi Wike a kan bayar da filaye a Abuj

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya buƙaci ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da kada ya ba shi wani fili a kyauta ko da ya nemi hakan.

Tinubu ya faɗi hakan ne a taron kungiyar lauyoyin Najeriya (NBA) na shekara-shekara a Abuja.

A maimakon haka, shugaban ya ja hankalin Wike da ya bayar da fifiko wajen kammala aikin hanyoyin cikin birnin Abuja domin ci gaban mazaunan birnin.

Yayin da yake gabatar da jawabin, Tinubu ya bayyana ministan babban birnin tarayya Abuja, a matsayin “mai gidan Abuja”.

Tinubu ya ce. manufarsa ba wai ya samu filaye kyauta ba ne, amma ya tabbatar da an samar da jirgin ƙasa wanda zai riƙa jigilar al’umma a birnin.

Wike dai ya riƙa haifar da muhawara tun bayan zama minista sakamakon alwashin da ya ci na rusa gine-ginen da aka yi ba bisa ƙa’ida ba.

Ministan, yayin ziyarar gani da ido a ranar Laraba, ya ce ya kamata a kammala aikin layin jiragen kasa na Abuja (ARMT) nan da watanni takwas.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp