fidelitybank

Tinubu ya gargadi masu kamfanin Siminti su mayar da farashinsa na baya

Date:

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umurci kamfanonin siminti a Najeriya da su koma kan tsohon farashin kayayyaki a lokacin da ake kara tsadar kayayyaki.

David Umahi, ministan ayyuka ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis bayan ya duba kamfanin siminti na BUA a jihar Sokoto.

Umahi ya ce, “Shugaban kasa ya dage da cewa su koma yadda suke a halin da ake ciki dangane da wannan farashin siminti na talaka.

“Ina so in ba su kwarin guiwa da su bi umarnin shugaban kasa domin mu cimma gagarumin shirin samar da gidaje da kuma sabon tsarin bege na sabbin hanyoyi na shugaban kasa,” in ji shi.

Buhunan siminti sun kai N10,000 da 15,000 a Abuja daga N5,000.

A wajen siminti kuma, farashin sauran kayayyakin gini ya yi tashin gwauron zabi.

A watan da ya gabata ne gwamnatin Najeriya ta bakin ministan gidaje da raya birane Ahmed Dangiwa, ta yi barazanar bude kan iyakokin kasar domin shigo da siminti idan masana’antun suka gaza rage farashin kayayyaki.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp