fidelitybank

Tinubu ya gargadi Malaman Addini da su shiga taitayin su

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya yi kira ga malamai da shugabannin addini da su guji “ƙasƙantarwa da kuma la’antar ƙasar” a cikin wa’azi kuma huɗubobinsu.

Tinubu ya yi kiran ne ranar Alhamis yayin da yake buɗe-baki tare da sarakuna da kuma jagororin addinin Musulunci da na Kirista a fadar shugaban ƙasa, yana mai jaddada cewa wa’azin da suke yi yana da matuƙar tasiri a cigaban ƙasar.

“Kishin ƙasar nan yana hannunku. Ku yi mata addu’a, ku ilimantar da yaranmu. Huɗubar da muke yi a masallatai da coci-coci na da matuƙar muhimmanci,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa: “Kada ku la’anci ƙasarku…Idan shugaba ba mutumin kirki ba ne ku bari zaɓe ya zo ku sauya shi, amma kada ku la’anci ƙasar. Da ma an tsara shugabanci ne da nufin kawo sauyi.”

Sarkin Zazzau Nuhu Bamalli ne ya wakilci Mai Alfarma Sarkin Musulmi Abubakar Sa’ad III a taron, wanda ya samu halartar Sakataren Ƙungiyar Kiristoci ta CAN Samson Fatokun.

Shi ma Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya nemi malaman da su “dinga haɗa kan al’umma don guje wa rikicin ƙabilanci da na addini”.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp