Shugaba Bola Tinubu a ranar Litinin, ya gargadi dansa, Seyi, da sauran mutane da su kaurace wa halartar ba taron majalisar zartarwa ta tarayya (FEC).
Tinubu ya bayyana karara cewa wadanda aka amince da su ne kawai ake ba su damar zama a taron majalisar ministocin na mako-mako.
“A makon da ya gabata, na lura da yadda mutane ke shiga da fita daga wannan majalisa ba bisa ka’ida ba.
“Na ga hoton ɗana, Seyi, zaune a baya. Wannan ba abin yarda ba ne.
“Zan sanar da ku mutanen da ya kamata su kasance a nan,” in ji shi.
Shugaba Tinubu ya ci gaba da bayyana sunayen masu ba shi shawara na musamman kan harkokin siyasa, Hadiza Usman; Bayani da Dabaru, Bayo Onanuga; Babban Sakatare mai zaman kansa, Hakeem Muri-Okunola da Sakatare mai zaman kansa, Damilotun Aderemi.
“Waɗannan su ne mutanen da aka keɓe don kasancewa a nan lokacin da muke gudanar da kasuwancin ƙasar. Sai dai in na aika a kira ku, kar ku zo, ku bayyana a sarari,” in ji Tinubu.